Posts

Showing posts from 2011

AMFANIN BANKIN MUSULUNCI

FASSARAR HUDUBA DAGA MASALLACIN SHEIK JA'AFAR MAHMUD ADAM, TUDN MURTALA KANO, 30/7/1432=1/7/2011. Dukkan yabo da godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, shi ne mafi sanin abin da kowanne dan Adam ke boyewa a zuciyarsa da abinda yake bayyanawa ina gode masa ina jinjina masa. Dukkan salati ya tabbata ga manzon Allah s.a.w shugaban dukkan halitttu gaba daya, wanda shine mai ceton kowa da kowa. Bayan haka yaku jama’a kuji tsoran Allah ku tsoraci dalilan saba masa da azabarsa ku bar abin da Allah yace ku bari matukar dai ku muminai ne. ku bar cin riba don tana daga cikin abin da yake jawo fushin Allah , tana daga cikin manyan laifuka masu halakarwa.

JUMA’A BABBAR RANA Falalarta Da Hukunce-Huukuncenta

Godiya ta tabbata ga Allha (Subahanahu WA Ta’ala). Tsira da Aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, Manzo Allha (salallahu Alaihi Wa sallam) da Alayensa da sahabbansa da wadanda suka bi tafarkinsu har zuwa ranar kiyama. Bayan haka: Na yi tunanin rubuta wannan littafi ne saboda da duba da yadda mafi yawan Musulmi suka jahilci girman wannan rana, da abin da ta kunsa na falaloli da darajoji da hukunce-hukunce, wadanda saninsu yana da mutukar amfani ga duk wani Musulmi. Don haka na yi kokarin in ga na fadi mafi yawancin abin daya kamata a sani a takaice, sauran abubuwan kuwa masu zurfi na yi nuni ga mai karatu zuwa ga wuraren da zai same su,