Posts

WAJABCIN HATTARA DA FITINU

Hudubar Juma'a  Daga Masallacin Sayyidina Abu Huraira Radiyallahu Anhu, Sokoto. An gabatar da ita a ranar jum’ah 16 Ga Muharram 1431H Daga Bakin Dr. Mansur Sokoto BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Fitina ita ce jarrabawa wadda dan adam yake gamuwa da ita a kodayaushe cikin rayuwa. Wannan jarabawar ga mummuni alheri ce, domin ta kan bayyana matsayin imaninsa da yardarsa ga Allah madaukakin sarki. Allah Ta’ala yana cewa: A.L.M. Shin mutane na tsammanin a kyale su su ce sun yi imani kuma ba a fitine su ba? Hakika mun fitini wadanda suka gabace su, sai fa Allah ya bayyana wadanda suka yi gaskiya kuma ya bayyana makaryata. Suratul Ankabut: 1-3. Jarrabawar

AL WALA’U WAL BARA’U

Fassarar Khudubar Juma'a daga masallacin Abu huraira(R)        An gabatar da ita a ranar juma’a 2 nd  Safar 1432 A.H Daga bakin Dr. Mansor Sokoto BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Ya al’ummar musulmi! Hudubarmu ta yau tana magana ne a kan wasu akidu guda biyu na musulunci da ake kira  Wala’a  da  Bara’a. Wala’a na nufin son wanda Allah ke son a so, Bara’a kuma tana nufin kin wanda Allah ke son a ki. Abinda aka sani ga mumini shi ne yana son Allah, yana kuma son masoyan Allah; yana kaunar su, yana taimakon su. Haka kuma yana kin duk abin da Allah ke ki da wadanda Allah ke ki da duk wata dabi’a ko aikin da Allah ke ki. Don haka ne Allah ya sifaita su da cewa, ba su tsoron zargin masu zargi a kan sha’anin Allah. Kuma Manzon Allah  Sallallahu Alaihi Wa Alihi Wasallam  ya sanya wannan akida

AMFANIN BANKIN MUSULUNCI

FASSARAR HUDUBA DAGA MASALLACIN SHEIK JA'AFAR MAHMUD ADAM, TUDN MURTALA KANO, 30/7/1432=1/7/2011. Dukkan yabo da godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, shi ne mafi sanin abin da kowanne dan Adam ke boyewa a zuciyarsa da abinda yake bayyanawa ina gode masa ina jinjina masa. Dukkan salati ya tabbata ga manzon Allah s.a.w shugaban dukkan halitttu gaba daya, wanda shine mai ceton kowa da kowa. Bayan haka yaku jama’a kuji tsoran Allah ku tsoraci dalilan saba masa da azabarsa ku bar abin da Allah yace ku bari matukar dai ku muminai ne. ku bar cin riba don tana daga cikin abin da yake jawo fushin Allah , tana daga cikin manyan laifuka masu halakarwa.

JUMA’A BABBAR RANA Falalarta Da Hukunce-Huukuncenta

Godiya ta tabbata ga Allha (Subahanahu WA Ta’ala). Tsira da Aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, Manzo Allha (salallahu Alaihi Wa sallam) da Alayensa da sahabbansa da wadanda suka bi tafarkinsu har zuwa ranar kiyama. Bayan haka: Na yi tunanin rubuta wannan littafi ne saboda da duba da yadda mafi yawan Musulmi suka jahilci girman wannan rana, da abin da ta kunsa na falaloli da darajoji da hukunce-hukunce, wadanda saninsu yana da mutukar amfani ga duk wani Musulmi. Don haka na yi kokarin in ga na fadi mafi yawancin abin daya kamata a sani a takaice, sauran abubuwan kuwa masu zurfi na yi nuni ga mai karatu zuwa ga wuraren da zai same su,